Magoya Bayan NNPP Sun Gabatar Da Sallah Don Neman Nasara Ga Abba Gida Gida A Kotu

Magoya Bayan NNPP Sun Gabatar Da Sallah Don Neman Nasara Ga Abba Gida Gida A Kotu

  • Dubban magoya bayan jam'iyyar NNPP a Kano sun sake gudanar da salloli don neman nasara a kotun zabe
  • Jam'iyyar APC a jihar Kano na kalubalantar zaben da aka gudanar a watan Maris na gwamna a jihar
  • Wannan ba shi ne karon farko ba da jam'iyyar NNPP ke gabatar da addu'o'i don samun nasara a kotu

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Kano - Magoya bayan jam'iyya mai mulki ta NNPP a jihar Kano sun gabatar da addu'o'i don samun nasara a kotu.

Jam'iyyar adawa ta APC ta shigar da kara kan tafka magudin zaben gwamnan da aka gudanar a watan Maris.

Magoya bayan NNPP a Kano sun yi addu'o'in neman nasara ga Abba Kabir
An gabatar da addu'o'in neman nasara ga Abba Kabir a Kano. Hoto: Daily Post.
Asali: Facebook

Me ye dalilin addu'o'in a Kano?

An gudanar da addu'o'in ne da kuma salloli don samun nasarar Gwamna Abba Gida Gida a shari'ar da ake na zaben gwamna.

Kara karanta wannan

Jerin Ministocin Tinubu Da Kotun Zabe Ta Ayyana a Matsayin Wadanda Suka Lashe Zaben Yan Majalisun Tarayya

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Addu'o'in na musamman an gabatar da su ne a kan hanyar Maiduguri da Hadejia da Zaria da Katsina da Gwarzo da kuma hanyar Madobi.

Yayin da ake dakon jiran yanke hukuncin daga kotu, magoya bayan Kwankwasiyya sun gabatar da sallar ce don neman taimakon ubangiji, cewar Tribune.

Sallar ta samu halartar manyan 'yan siyasa da kuma da mukarraban gwamnati da kuma magoya baya.

Hajiya Zuwaura Abubakar, shugabar mata ta NNPP, ta bayyana cewa addu'o'in an shirya su ne kan masu neman kwace kujerar gwamna ba tare da adalci ba.

Meye mutane ke cewa kan addu'o'in a Kano?

Ta ce mutanen na shirye-shiryen zaluntar Gwamna Abba Kabir a shari'ar da ake a kotun kan zabe, The Guardian ta tattaro.

Ta ce:

"Wannan salla an yi ta ne saboda ma su kisa tarwatsa nasarar Gwamna Abba Kabir a kotun zabe."

Kara karanta wannan

Ga ci ga rashi: An kwace kujerar sanatan PDP a Arewa, an ba wani fitaccen tsohon gwamnan APC

Wannan ba shi ne karon farko ba da magoyan bayan NNPP ke gabatar da salloli don neman nasara.

Abba Kabir ya kori shugabannin makaranta 2 a Kano

A wani labarin, Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kori wasu shugabannin makarantun sakandare guda biyu a jihar.

Gwamnan ya dauki matakin ne saboda wasa da aiki da akae zargin shugabannin da aikata wa a wurin aikinsu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel