Yan Ta’adda Sun Hallaka Wani Fitaccen Malamin Addinin Musulunci A Gombe

Yan Ta’adda Sun Hallaka Wani Fitaccen Malamin Addinin Musulunci A Gombe

  • Wasu da ake zargin barayi ne sun yi ajalin fitaccen malamin addinin Musulunci a jihar Gombe a daren jiya Talata a gidansa
  • Marigayin mai suna Ibrahim H. Musa da aka fi sani da Albanin Kuri ya kasance fitaccen matashin malami da ke wa'azi a jihar
  • Shugaban Kungiyar JIBWIS ta jihar Gombe, Injiniya Salisu Muhammad ya sanar da lokacin sallar jana'izar marigayin

Jihar Gombe - Wasu 'yan ta'adda sun yi wa shahararren malamin addinin Musulunci, Sheikh Ibrahim Musa da aka fi sani Albanin Kuri kisan gilla a gidansa da ke Gombe.

'Yan ta'addan sun kai wa marigayin farmaki ne a daren Talata 8 ga watan Agusta a gidansa da ke cikin garin Gombe yayin da su ka je yin sata.

Barayi sun yi ajalin malamin Musulunci a jihar Gombe bayan artabu a daren jiya Talata
Sheikh Musa Ibrahim Da Aka Fi Sani Da Albanin Kuri Wanda Barayi Su Ka Masa Kisan Gilla A Gombe. Hoto: Facebook.
Asali: Facebook

An saka lokacin sallar jana'izar malamin a Gombe

Kara karanta wannan

Kisan Albanin Kuri: Iyalan Malamin Da Aka Kashe Sun Bayyana Halin Da Suke Ciki, Sun Ba Da Sako Ga Gwamnati

Ana sa ran gudanar da sallar jana'izarsa da misalin karfe 1:00 na rana a masallacin Bolari da ke cikin birnin Gombe, Aminiya ta tattaro.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Wata majiya ta tabbatar da cewa ana zargin barayi da kisan malamin inda suka yi artabu da shi kafin suka sassara shi a jiki tare da yanka wuyansa a daren Talata 8 ga watan Agusta.

Wani da bai bayyana sunansa ba ya ce ya je har kan gawar marigayin inda ya ce barayin sun sassara shi a jiki da kuma wuyansa bayan sun yi gwagwarmaya da barayin a gidansa.

Meye rundunar 'yan sanda ta ce?

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, Mahid Mu'azu ya ce ba shi da masaniya a kan abin da ya faru amma zai fitar da bayani bayan samun cikakken rahoto kan kisan malamin, WikkiTimes ta tattaro.

Kara karanta wannan

Kaduna: Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Malamin Musulunci, Matarsa Da Yara 2, Ciki Harda Jaririn Kwana Daya

Marigayi Albanin Kuri na daga cikin malaman addini musamman na Musulunci a Najeriya da aka musu kisan gilla da suka hada da Sheikh Ja'afar Mahmud Adam da Sheikh Muhammad Auwal Adam Albani Zariya.

A martanin shi, yayan malamin mai suna Halliru Dahiru ya fadawa Legit.ng Hausa cewa malamin ya yi neman gafara a wurin mutane tare da musu nasiha da su rike salatin Annabi.

Ya ce:

"Tabbas mun yi rashin malam don kullum cikin aikin Allah, inda ya ce ana saura kwanaki uku ya rasu ya nemi yafiyan mutane.
Mu 'yan uwan malam ba mu yafe ba, duk da shi malam kafin ya rasu ya ce ya yafe amma mu jinin malam ba mu yafe ba.

Jimami: Allah Ya Yi Wa Mai Martaba Yariman Gombe Rasuwa Yana Da Shekara 77

A wani labarin. an shiga jimami yayin da Yariman Gombe, Alhaji Abdulkadir Abubakar ya riga mu gidan gaskiya a ranar Talata 1 ga watan Agusta a birnin Gombe.

Kara karanta wannan

Ya ake ciki? An fadi yanayin da Bazoum ke ciki bayan ganawarsa da likitansa

Marigayi Yariman Gombe ya rasu ya na da shekaru 77 da yammacin ranar Talata ana daf da shiga sallar magariba bayan fama da doguwar jinya.

Marigayin wanda baffa ne a wurin Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Abubakar Shehu Abubakar 111 ya rasu ne a unguwar Tudun Wada da ke birnin Gombe inda ya bar mata guda biyu da 'ya'ya da dama.

Asali: Legit.ng

Online view pixel