Gabanin zaben 2023: Tinubu ya ba jami'a kyautar N1bn ana tsaka da yajin aikin ASUU

Gabanin zaben 2023: Tinubu ya ba jami'a kyautar N1bn ana tsaka da yajin aikin ASUU

  • Tsohon gwamnan jihar Legas, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya ba da gudummawar Naira biliyan 1 don gina cibiyar jagoranci a jami’ar jihar ta Legas
  • Mataimakin shugaban jami'ar ta jihar Legas ne ya sanar da bayar da gudummawar a lokacin taron yaye dalibai na jami'ar karo na 25
  • Tinubu ya jagoranci al’amuran jihar Legas daga 1999 zuwa 2007 kuma tun daga nan ya zama shugaban jam’iyyar APC na kasa

Dan takarar shugaban kasa kuma jigo a jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya baiwa jami’ar jihar Legas (LASU), gudunmawar kudi don gina wata cibiyar bunkasa ilimin jagoranci da ya kai Naira biliyan 1.

Mataimakin shugaban jami'ar LASU, Farfesa Ibiyemi Olatunji-Bello ne ya sanar da bayar da gudummawar a taron laccar yaye dalibai karo na 25 a ranar Alhamis, 24 ga watan Maris.

Kara karanta wannan

Mu ya mu: ‘Yan takarar shugaban kasa na PDP sun gana don zaban daya kwakkwara

Tinubu ya zubar da kudi a jami'ar Legas
Shirin zaben 2023: Tinubu ya ba jami'a kyautar N1bn duk da ana yajin aikin ASUU | Hoto: Pius Utomi Ekpei/AFP
Asali: Getty Images

Jaridar Leadership ta ruwaito cewa, mataimakin gwamnan jihar Legas Dr. Obafemi Hamzat ne ya wakilci Tinubu a wajen taron.

Da yake magana ta bakin Hamzat, Tinubu ya bukaci gwamnati ta tallafa wa masana’antun dabaru da za su dauki matasa aiki tare da samar da ayyukan yi.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya ce tallafin da gwamnati ke bayarwa na kere-kere da masana’antu zai kara bude kofa ga fara sana’o’in da kasuwanci tsakanin matasa.

A fadinsa:

"Manufofin masana'antu da ayyukan yi na kasa dole ne su yi tashi daga shafukan takardu su zo cikin rayuwa ta zahiri.
“Wannan zai taimaka wajen gyara al’umma don inganta tattalin arzikin matasa a cikinta.
"Muna bukatar sabuwar hanya mai gamsarwa, hanyar da za ta ba ku dama mai kyau a kyakkyawar damar samun wadata mai dorewa."

Wadanda suka halarci taron a jihar Legas

Kara karanta wannan

Da dumi-dumi: Fayemi ya yi watsi da batun goyon bayan yan takarar da Buhari ke so

Wadanda suka halarci bikin sun hada da Gwamna Abdullahi Ganduje na jihar Kano, da wakilan gwamna Aminu Masari na jihar Katsina, da mataimakin gwamnan jihar Borno, da mataimakan shugabannin jami'o'i daban-daban na kasar nan.

Haka kuma, akwai tsoffin gwamnonin jihar Legas biyu, Gimbiya Adejoke Adefulire da Dr Idiat Adegbule, kamar yadda Independent ta ruwaito.

A bangare guda, Jami’ar Jihar Legas ta nada Farfesa Peter Okebukola ado a matsayin Farfesa Emeritus.

Bidiyon Wasu Matasa Suna 'Kaca-Kaca' Da Fuskar Tinubu a Hoto Ya Bazu a Dandalin Sada Zumunta

A wani labarin, wani bidiyo ya bayyana a dandalin sada zumunta. Bidiyon ya nuna wasu matasa suna zanga-zanga suna lalata fuskar Bola Ahmed Tinubu, jigon jam'iyyar APC na kasa kuma dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar.

Ana kyautata zaton an nadi bidiyon ne a lokacin zanga-zangar Endsars. A lokacin, jami'an tsaro sun bude wuta ga wasu yan Najeriya a Lekki Toll Gate.

Kara karanta wannan

Allah ya zabi Tinubu ya gaji Buhari: Malaman addinin kirista a Arewa sun ce an yi musu wahayi

Tinubu, saboda matsayinsa na fitaccen mai goyon bayan gwamnati mai ci yanzu ya sha suka daga wurin masu zanga-zangar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel