Karin bayani: Bayan rugujewar gini, mummunar gobara ta kone gine-gine a Legas

Karin bayani: Bayan rugujewar gini, mummunar gobara ta kone gine-gine a Legas

  • A jihar Legas, sun sake samun wani mummunan hadarin da yayi sanadiyyar konewar dunkiyoyi
  • An samu tashin gobarar ne kwanaki kadan bayan da wani ginin bene mai hawa sama da 20 ya ruguje
  • Matasa sun fusata bisa makarar zuwan jami'an kashe gobara, lamarin da ya kai ga suka afkawa jami'an

Legas - An samu hargitsi a ranar Laraba, 3 ga watan Nuwamba, yayin da wata gagarumar gobara ta cinye wasu gine-gine da shaguna a Owode Onirin, daura da unguwar Ikorodu Road a Legas.

Vanguard ta rahoto cewa a lokacin da jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Legas, suka isa wurin da lamarin ya faru, wasu fusatattun matasa sun far musu.

An ce matasan sun kai wa jami’an hari ne saboda rahotanni sun ce sun isa wurin a makare bayan an yi ta kiran su yayin da wutar ta kama.

Kara karanta wannan

Gwamnan Legas ya je wurin da bene ya ruguje domin ganewa idonsa abin da ya faru

Yanzu-Yanzu: Bayan rugujewar gini, wata mummunar gobara ta kone gidaje da shaguna a Legas
Taswirar jihar Legas | Hoto: naijanews.ng

Wannan ya sanya wutar ta tashi zuwa gine-ginen da ke kusa.

Hukumar kashe gobara ta jihar, Sakiru Amodu, ya tabbatar da barkewar gobarar, inda ya ce ana kokarin kashe gobarar.

Gwamnan Legas ya je wurin da bene ya ruguje domin ganewa idonsa abin da ya faru

Jaridar Punch ta ruwaito cewa, gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu ya isa wurin da ginin bene mai hawa 22 a Ikoyi ya ruguje.

Rahotanni sun nuna cewa Sanwo-Olu ya ziyarci wurin da lamarin ya faru a yau da misalin karfe 1 na rana.

Kafin isowar gwamnan, an fitar da wasu gawarwaki biyu daga baraguzan ginin da ya ruguje, wanda ya kawo adadin wadanda suka mutu zuwa 22, PM News ta ruwaito.

Yadda manyan gine-gine 8 suka ruguje a Najeriya cikin shekaru 15

Kara karanta wannan

Rahoto: Yadda gobara ta kone mutane 10 tare da lalata miliyoyi a Kano

A wani labarin, Za a iya tunawa da rugujewar wani babban bene a ranar Litinin, 1 ga Nuwamba, 2021, a matsayin wata rana mai muni ga 'yan Najeriya.

Ginin da ya ruguje a titin Gerald da ke unguwar Ikoyi, wuri ne da ake gina gidaje na alfarma.

Sai dai abin takaici, ba wannan ne karon farko da ‘yan Najeriya ke fuskantar irin wanna, ba, suna mamakin ko me aka yi don hana rugujewar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel