Tuna Baya: Yadda Wani ‘Dan Majalisa a Birtaniya Ya Jefi Janar Gowon Da Wawurar Baitul-Mali

Tuna Baya: Yadda Wani ‘Dan Majalisa a Birtaniya Ya Jefi Janar Gowon Da Wawurar Baitul-Mali

  • Wani ‘Dan Majalisar Birtaniya ya zargi Janar Yakubu Gowon da laifin sata
  • ‘Dan Majalisar ya ce tsohon Shugaban kasar ya saci kudi daga asusun CBN
  • Babu abin da zai iya tabbatar da wannan magana da ‘Dan siyasar Turan ya yi

Birtaniya - Wani ‘dan majalisar Birtaniya, ya fito ya na ikirarin cewa tsohon shugaban kasar Najeriya na mulkin soji, Yakubu Gowon, ya saci kudin al’ummarsa.

‘Dan majalisar ya bayyana wannan ne gaban wani zaure, inda ya jefi Janar Yakubu Gowon mai ritaya da laifin awon gaba da rabin kudin CBN.

An zargi Janar Gowon da tafka sata
Dan majalisar Birtaniya ya zargi Yakubu Gowon da satar rabin kudin CBN. Hoto: @NTANewsNow
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ke cewa “Mun san yadda Janar Yakubu Gowon ya yi awon-gaba da rabin dukiyar da ke cikin babban bankin Najeriya (CBN), ya tsere Landan.”

Kara karanta wannan

'Yan Bindga 67 Sun Baƙunci Lahira Yayin da Jami'ai Suka Ceto Mutane 20 da Aka Yi Garkuwa da Su a Bauchi

Wannan ‘dan majalisa bai kawo wasu hujjoji da za su gamsar da abin da ya yi da’awa ba, ya nuna rade-radi ya samu, ya ce:

“Kamar yadda ake fada.”

Sannan ya cigaba da cewa:

Mun san cewa a cikin birnin nan namu, abin ban haushi, akwai wasu dasu ka lamushe kudin mutanen Najeriya da aka sace.”
“Mun san ana amfani da bankunanmu wajen wannan aiki (wawuran dukiyar sata), don haka Ingila na da damar huro wuta a kan masu sace kudin Najeriya."

A nan ma wannan mutumi da Legit Hausa ba za ta iya tantancensa ba, bai ambaci sunayen mutanen da suke zaune a kan kudin talakawar Najeriyar ba.

Ko da cewa Najeriya ta samu makudan kudi a lokacin da Janar Yakubu Gowon ya yi mulki tsakanin 1966 – 1975, babu hujjar ya yi sata daga CBN.

A lokacin da aka kifar da Gowon daga mulki ya na Uganda, kuma daga nan ya zarce zuwa Ingila, amma ba a zarge shi da satar kudin bankin CBN ba.

Kara karanta wannan

Seyi Tinubu Ya Jawowa Mahaifinsa Suka Saboda Yawo a Jirgin Shugaban Kasa

A ranar 19 ga watan Oktoba, 2020, Janar Yakubu Gowon ya cika shekara 86 da haihuwa. A dalilin haka ne mu ka kawo gajeren tarihin tsohon shugaban.

Gowon ya yi karatu a makarantar sojoji ta Royal Military Academy Sandhurst, Ingila, Staff College, Camberley, da kuma Joint Staff College a garin Latime.

Yakubu Gowon: Ba gaggawa na ke in bar duniya ba

Janar Yakubu Gowon mai murabus, tsohon shugaban mulkin soja na Najeriya ya karyata jita-jitar cewa ya rasu.

Wasu kafafen watsa labarai sun wallafa hakan a dandalin sada zumunta a ranar Litinin amma hadimin Gowon ya fitar da sanarwar musanta hakan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel